19 Yuli 2015 - 12:38
Ashton Carter zai kai ziyara HKIsra'ila

Sakataren harkokin tsaron Amurka zai kai ziyara HKIsra'ila a yau inda daga bisani kuma zai wuce Saudia da kuma Jordan.

An bayyana ziyarar ta sa matsayin wata hanya ta kara samun dai-daito a tsakanin kasashen da suke da hannun a yarjejeniyar da aka cimma kan shirin Iran na makamashin nukiliya.

Ashton Carter zai kuma tattauna da jami'an HKIsra'ila kafin ya gana da firaminista Benjamin Natanyahu a ranar talata.

Tuni dai  Natantahu ya ce yarjejeniyar da aka cimma akan shirin Iran din anyi babban kuskure a tarihi.288